in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani kwararre dan Najeriya ya yabawa shirin yarjejeniyar kiwon lafiya na Sin da Afrika
2015-10-09 10:12:24 cri
Tsohon kwamishinan kiwon lafiya na jihar Ogun dake shiyyar kudu maso yammacin Najeriya Olaokun Soyinka, ya yabawa shirin yarjejeniyar kiwon lafiya na Cape Town Declaration tsakanin kasar Sin da jami'an kiwon lafiya na kasashen Afrika.

Soyinka, ya bayyana hakan a yayin zantawa da kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua a ranar Alhamis din nan a Abeokuta babban birnin jihar Ogun, ya ce aiwatar da wannan shirin tsakanin kasar Sin da Afrika zai yi matukar taimakawa fannin kiwon lafiya a fadin nahiyar ta Afrika.

Soyinka wanda tsohon jami'in hukumara lafiya ta duniya WHO ne, ya ce, tabbas wannan shirin zai taimakawa al'ummar nahiyar Afrika baki daya.

Ya kara da cewar wannan shirin zai yi matukar tasiri wajen musayar ilmi da fasaha a bangaren kiwon lafiya a nahiyar.

Sai dai jami'in ya kara da cewar, shirin zai fi amfani ne, idan ya kasance an gudanar da shi da zummar cin moriyar juna.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China