in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojin Najeriya ta ce ta hallaka 'yan ta'adda 100 a wata arangama
2015-10-08 09:41:56 cri
Sojojin Najeriya sun tabbatar da cewa sun hallaka 'yan ta'adda guda 100 a safiyar laraba a jihar Yobe dake arewa maso gabashin kasar. Kamar yadda kakakin sojin yankin Kanar Sani Kukasheka Usman ya bayyana a cikin wata sanarwa, ya ce 'yan ta'addan a kokarin da suka yi na tserewa ya sa suka yi arangama da sojojin a yankin Gondiri na jihar Yobe, daya daga cikin jihohin uku da 'yan ta'addan suka addaba kwanan nan.

Sai dai kakakin ya bayyana cewa a lokacin arangamar an kashe sojoji 7 bayan nasarar da suka yi a kan 'yan ta'addan sannan aka raunata sojoji 8.

Sojin Najeriyan ta bayyana cewa bayan dakile 'yan kungiyar sun kwato makamai masu yawan gaske da albarusai da sauran kayuayyaki da suka hada da bindiga komai da ruwan ka babba guda daya, da harsasin harbar roka guda biyu, da bindigar AK47 mai daure da harsasan NATO duk daga hannun 'yan ta'adda.

Makonni biyu da suka wuce fiye da 'yan ta'addan 200 suka mika wuya ga sojin kasar a garin Banki wani muhimmin garin da a baya 'yan ta'addan suka mamaye. Sojin na bayanin cewa sun hargitsa 'yan ta'addan a garuruwa da dama da unguwanni a jihohin Borno, Yobe da Adamawa duk a makonnin baya.

A wani labarin kuma sojojin kasar ta Nigeriya a Bama da Ngurosoye dake kusa da jihar ta Borno sun gano tare da hako wassu ababen fashewa da kungiyar ta boko haram suka binne, kamar yadda cibiyar tsaron kasar ta tabbatar.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China