in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi gargadi ga Sudan ta kudu da ta kula da lafiyar jami'an UNMISS dake kasar
2015-10-09 10:02:27 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya bukaci gwamnatin Sudan ta kudu da kada ta kuskura ta bari a sake cin zarafin tawagar jami'an ta dake aikin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudun wato UNMISS a takaice, kamar yadda aka cimma yarjejeniya tsakanin gwamnatin kasar da MDD.

Mai Magana da yawun kwamitin na MDD Stephane Dujarric, ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Alhamis din nan.

A ranar laraba ne dai, yayin da jami'an na UNMISS suka tashi daga babban birnin kasar Juba zuwa yankin Wonduruba, sojojin kwatar 'yancin Sudan wato SPLA suka tsayar da tawagar, sannan suka ci zarafin su har ma an lakadawa wasu daga cikin tawagar duka.

Sakamakon irin mawuyacin halin da jami'an na UNMISS suka fuskanta, ya sa dole suka juya baya suka koma Juba.

Dujarric ya ce, MDD ta yi Allah wadai da wannan al'amari, sannan ta bukaci a gaggauta gudanar da bincike domin gano wadanda ke da hannu domin hukunta su.

Kazaika MDD, ta bukaci gwamnatin Sudan ta kudu, ta kyale jami'an na UNMISS da su gudanar da aikin su kamar yadda aka cimma yarjejejniya tun da farko.

An dai kafa UNMISS a ranar 9 ga watan Yulin 2011 ne bayan samun 'yancin Sudan ta kudu, lamarin da ya kawo karshen basasa tsakanin arewaci da kudancin Sudan.

A tsakiyar watan Disambar shekarar 2013 ne dai, rikicin siyasa ya kaure tsakanin shugaban kasar Sudan ta kudun Salva Kiir, da mataimakin sa Riek Machar, lamarin da ya sake jefa kasar cikin wani sabon tashin hankali. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China