in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi maraba da yadda Kiir ya sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya
2015-08-27 10:28:05 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya yi maraba da yadda shugaba Salva Kiir na Sudan ta kudu ya sanya hannu kan yarjejeniyar kawo karshen tashin hankalin da aka kwashe kusan watanni 20 ana tabkawa a kasar.

Mr Ban wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa ta hannun kakakinsa ya bayyana cewa, wannan muhimmin mataki ne na kawo karshen tashin hankalin da ya cusa al'ummar kasar cikin akuba.

Babban sakataren MDDr ya kuma yaba wa kungiyar IGAD bisa kokarin ta na ganin kammalar tattaunawar cikin nasara. Mr Ban ya bayyana farin cikinsa kan hadin kan da shugabannin shiyyar suka nuna na ganin an kawo karshen wannan tashin hankali.

A makon da ya gabata ne shugaban 'yan tawaye Riek Machar ya sanya hannu kan yarjejeniyar yayin da shugaba Kiir ya ki sanya hannu a yarjejeniyar.

Sanya hannun da shugaba Machar din ya yi alama ce da ke nuna kawo karshen fadan da dakarun bangarori biyu ke yi, yayin da Riek Machar zai koma kan mukaminsa na mataimakin shugaban kasar Sudan ta kudun wadda ta samu 'yancinta a shekara 2011 daga kasar Sudan.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China