in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin da suka yi jiyin mulki a Burkina Faso sun ki amincewa da wa'adin karshe da aka ba su na mika wuya ga sojojin gwamnatin kasar
2015-09-23 10:00:00 cri
Jagoran sojojin da suka yi juyin mulki a kasar Burkina Faso Gilbert Diendere ya ki amincewa da wa'adia karshe da aka ba su a jiya Talata 22 ga wata na su mika kai ga sojojin gwamnatin kasar.

A cikin wata sanarwa da Diendere ya bayar a wannan rana, ya ce, idan sojojin da ke goyon bayan gwamnatin wucin gadi suka kai musu hari, su ma za su kare kansu. A sa'i daya kuma, ya ce, yana jiran sakamakon da aka cimma a taron gaggawa da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta ECOWAS ta shirya a birnin Abuja na tarayyar Nijeriya game da daftarin shiri da bangarorin daban daban na kasar suka daddale.

A ranar 20 ga wata, kungiyar shiga tsakani ta ECOWAS da wakilan zaratan sojojin da ke gadin fadar shugaban kasar Burkina Faso suka cimma ra'ayi guda game da daftarin shiri a birnin Ouagadougon da ke kasar, don kawo karshen tashe-tashen hankali, da yin afuwa ga sojojin da suka shirya juyin mulkin, kana za a mika mulki ga gwamnatin wucin gadin kasar, gami da shirya zaben majalisar dokoki da babban zaben kasar a ranar 22 ga watan Nuwamba.

Rahotanni na cewa, an kai shugaban wucin gadin kasar Michael Kafando da sojojin da suka shirya juyin mulkin zuwa ofishin jakadancin kasar Faransa dake kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China