in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An maido da gwamnatin wucin gadi bayan juyin mulki da akayi a Burkina faso
2015-09-23 21:50:20 cri
Rahotanni daga birnin Ouagadougou na kasar Burkina fasoi ya tabbatar da cewar Shugaban wucin gadi na kasar Micheal Kafando yayi jawabi ta kafofin watsa labarai cewar an maido da gwamnatin wucin gadi.

Yace tun daga ranar Alhamis gwamnatin wucin gadin zai cigaba da aiwatar da ayyukan shi yadda ya kamata.

Kagfando wanda yake cikin wadanda aka kame a makon jiya lokacin juyin mulkin kafin a sako shi ya gode ma al'ummar kasar wadanda suka tabbatar da ganin yunkurin juyin mulkin da rundunar tsaron shugaban kasar suka yi na makon jiya yaci tura.

A daren tarlatan jiya ne bangaren sojojin da suka yi yunkurin juyin mulkin dana bangaren masu biyayya da gwamnati wadanda ke barazanar mai da martani tsakani suka rattaba hannu akan yarjejeniyar kawo karshen duk wata barazana da suke ma junan su.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China