in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya mutane 56 sun rasa rayukan su sakamakon dauki ba dadi tsakanin sojoji da 'yan Boko Haram
2014-07-07 16:45:54 cri
Rundunar sojin Najeriya ta ce dauki ba dadin da jami'an ta suka yi da magoya bayan kungiyar nan ta Boko Haram, a garin Damboa na jihar Borno ta sabbaba rasuwar mutane 56.

Wata sanarwa da kakakin rundunar sojin ta Najeriya manjo janar Chris Olukolade ya fitar, ta bayyana cewa dauki ba dadin na ranar Juma'a, ya biyo bayan yunkurin da 'yan Boko Haram din suka yi ne, na aukawa barikin soji da kuma wani caji ofis dake Damboa, lamarin da ya sabbaba musayar wuta tare da kisan 'yan Boko Haram din su 50, da sojoji 5, tare da wani hafsa daya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China