in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta farma 'yan ta'adda a maboyarsu tare da kashe 'yan kungiyar a kalla 44
2014-07-08 20:46:05 cri
Rundunar Sojan Najeriya a ranar litinin din nan ta sanar da kai wani samame na kasa da sama a sansanin 'yan kungiyar nan ta Boko Haram dake jihar Borno a arewa maso gabashin kasar inda ta samu nasarar kashe sama da 'ya'yan kungiyar 44.

Kakakin rundunar sojin kasar Manjo Janar Chris Olukolade wanda ya tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da kamfanin dillanci labarai na kasar Sin Xinhua ta samu ya ce rundunar sojin kasar sun kawar tare da kwato dajin Balmo a wani samame da suka kai a wanda ya dauki daukacin karshen makon da ya kare.

Ya ce kafin wannan aiki Dajin Balmo wanda ya mika har cikin jihohin Bauchi da Jigawa yana hannun 'yan ta'addan ne inda suka mayar da shi sansani da maboyar su suna kai hare hare a kan al'umma.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China