in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso : Masu shiga tsakani da sojoji sun cimma matsaya guda kan maido mulkin wucin gadi
2015-09-21 10:09:00 cri
Sojojin da suka yi juyin mulki a kasar Burkina Faso da masu shiga tsakani na kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) da alamun sun cimma matsaya daya, a ranar Lahadi a birnin Ouagadougou, domin maido da mulkin rikon kwarya da Michel Kafando ke jagoranta.

Sojojin da suka yi juyin mulki sun tsare shugaban rikon kwarya Michel Kafando, a ranar Laraba, kafin daga baya su sake shi a ranar Jumma'a.

Masu ruwa da tsaki a fagen siyasa da kuma masu shiga tsakani na kungiyar ECOWAS da ma gamayyar kasa da kasa sun cimma na kada kuri'ar bada afuwa da dukkanin sojojin da suka yi juyin mulki na ranar Laraban da ta gabata. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China