in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Angola ta yi kiran da a cimma yarjejeniyar sauyin yanayin da za ta taimakawa kasashe masu tasowa
2015-10-02 13:39:02 cri
Mataimakin shugaban kasar Angola Manuel Domingos Vincente Kasar ya yi kira ga mahalarta taro kan sauyin yanayi da zai gudana a birnin Paris a watan Disamba, da su cimma sabbin yarjejeniyoyin da za su kasance masu fa'ida ga kasashe masu tasowa.

Manuel Domingos Vincente ya yi wannan kiran a jiya lokacin da yake jawabi a rana ta hudu na babban taron muhawara na MDD.

Ya ce, matsalar canjin yanayi tana daya daga cikin kalubalen da dan-Adam ke fuskanta a wannan duniya, don haka kamata ya yi masu ruwa da tsaki a taron Paris kan canjin yanayi, su yi kokarin bullo da matakan da za su kasance masu tasiri ga kasashe masu tasowa.

MDD ce za ta jagoranci kokarin da kasashen duniya ke yi na ganin an cimma yarjejeniyar yaki da matsalar sauyin yanayi a taron na Paris. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China