in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a yi hadin gwiwar yakar ta'addanci bisa ka'idojin MDD
2015-10-01 13:12:40 cri
A jiya Laraba ne Mr. Wang Yi, ministan harkokin wajen kasar Sin wanda ya halarci taron ministoci na kwamitin sulhu na MDD kan batun tinkarar rikice-rikice da ayyukan ta'addanci da ke faruwa a yankin Gabas ta tsakiya da Arewacin Afirka ya bayyana matsayin da kasar Sin ke dauka kan batun yakar ta'addanci cikin hadin gwiwa tsakanin kasa da kasa.

Wang Yi ya nuna cewa, ta'addanci abokin gaban bil Adam ne, don haka bai kamata a yi amfani da ma'aunai biyu wajen yakar ayyukan ta'addanci ba. Ayyukan yakar ta'addanci na amfani da nuna karfin tuwo iri daban daban ya kamata ya zama abu mai muhimmanci ga kasashe da gamayyar kasa da kasa.

Daga bisani Wang Yi ya bayar da shawara cewa, kasar Sin tana fatan kasashen duniya za su hada kai bisa ka'idojin MDD wajen yakar ta'addanci daga dukkan fannoni, musamman a ayyukan ta'addanci da ake yi a shafukan intanet, da yin rigakafin yaduwar tsatsauran ra'ayin nuna karfin tuwo, da yunkurin toshen hanyar da 'yan ta'addan ke samun kudi da sauran tallafi da kara yin musayar bayanan sirri don yakar ayyukan ta'addanci, kana MDD ta kara taka rawa kamar yadda ya kamata. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China