in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-haren da Rasha ta kai ta jiragen sama ya lalata mafakar kungiyar IS a Syria: in ji ministan tsaron kasar
2015-10-01 13:09:11 cri
Ministan tsaron Rasha ya fada a ranar Laraba cewar, wasu jerin hare-hare ta jiragen sama da Rashan ta kai kimanin 20 kan mayakan kungiyar IS a Syria ya illata maboyar 'yan kungiyar ciki har da wata babbar cibiyar mayakan na IS.

Mai magana da yawun ma'aikatar tsaron Rasha Igor Konashenkov, ya ce harin bai shafi yankunan fararen hula ba.

Mai magana da yawun hukumar tsaron na Kremlin, Dmitry Peskov, ya ce wannan hari da Rasha ta kai ta sama a Syria na wucin gadi ne, kuma za'a ci gaba da kai harin ne kadai a lokacin da dakarun gwamnatin Syria ke yin lugudan wuta a yankunan.

Peskov ya bukaci kasashen duniya da wannan lamari ya shafa da su watsa bayanai da suka shafi yaki da ta'addanci a tsakanin su.

Kasar ta Rasha ta yanke shawarar kaddamar da hare hare ta sama ne kan mayakan IS a Syria, bayan da majalisar dokokin kasar ta amince da shugaba Vladimir Putin da ya yi amfani da sojojin sama wajen kai hare haren a Syria a ranar Larabar nan.

Bayan 'yan sa'o'i da kaddamar da harin na farko, fadar White House ta Amurka ta jaddada aniyar hada kai da Rasha domin kawo karshen rikicin Syria. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China