in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Etoile ta lallasa Zamalek a gasar cin kofin CAF
2015-09-29 16:03:44 cri
Kulob din Etoile Sahel na kasar Tunisia ya lallasa Zamalek na kasar Masar da ci 5 da 1 a wasan da ya gudana tsakaninsu a Sousse na kasar Tunisia a ranar Lahadin da ta gabata, hakan ya tabbatarwa Etoile matsayin ta na kulob da zai halarci wasannin zagayen karshe na gasar CAF Confederation Cup. A wajen wasan, dan wasan Etoile Marouane Tej ya zara kwallaye 2 cikin raga, yayin da takwarorinsa Baghdad Bounedjah, da Alaya Brigui, da Saddam Ben Aziza, dukkansu suka zara kwallaye daya-daya.

A nashi bangare, dan wasan kulob din Zamalek Ayman Hefny, ya samu damar mayar zara kwallo daya cikin ragar Etoile, bayan da aka rigaya aka zara kwallaye 2 cikin ragar kulob din kasar Masar. Sai dai Zamalek ya tsaya a nan bai sake taka wata rawar a-zo-a-gani ba a wasan.

Idan an waiwayi wasanni 3 da aka kammala bugawa a matsayin wasannin rukunai a wannan kakar wasan, za a ga Etoile ta samu maki 4,wanda kuma yana cikin wani yanayi mai kyau da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin kulob din. Yayin da a nasu bangare 'yan wasan kulob din Zamalek sun samu maki 3 kawai, inda har Orland Pirates na kasar Afirka ta Kudu ya lashe kulob din da ci 4 da 1 a wasan da ya gudana tsakaninsu makwanni 2 da suka wuce.

An samu sakamakon wasan ne wasu sa'o'i 24 bayan da Pirates ya lashe Al Ahly, wani kulob din Tunisia mai karfi ne, da ci 1 da ba ko daya, a birnin Soweto na kasar Afirka ta Kudu.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China