in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan wasan damben kasar Uganda ya lashe lambar tagulla a gasar AAG
2015-09-17 13:22:20 cri
Kasar Uganda ta lashe lambar tagulla ta biyu a gasar wasannin motsa jiki ta nahiyar Afirka da yanzu haka ke gudana a kasar Congo, bayan da Kennedy Katende dan wasan damban Boxing na Uganda, ya sha kashi hannun takwaransa Benchelba Abdelhafid na kasar Algeria a wasan kusa da na karshe ajin masu nauyi da aka fafata a ranar Asabar din karshen mako.

Kafin lambar tagullar da Katende ya samu, shi ma dan wasan badminton na kasar Edwin Ekiring, ya lashe irin wannan lamba a wasan kusa da na karshe ajin maza da ya buga shi da dan kasar Afirka ta kudu wanda yayi nasara a wasan.

Duk dai da matsayin da 'yan wasan na Uganda suka samu bai kai matakin koli ba, Katende ya ce yayi farin ciki da tagullar da ya samu. Ya ce gwabzawar da suka yi da takwaransa na Algeria ta bashi damar sake gogewa, tare da sake fahimtar dabarun wasan na dambe.

Benchelba Abdelhafid na Algeria ya taba kaiwa wasan zagayen gasar har sau biyu a baya. Da kuma wannan nasara ta lashe lambar tagulla da 'yan Ugandan biyu suka samu, kasar ta daga zuwa matsayi na 20 sama da kasar Mali da tagulla biyu, yayin da kuma Masar ta ci gaba da mamaye gasar da lambobi 130 wadanda su ne mafiya yawa a gasar, kana Afirka ta Kudu ke biye mata a matsayi na biyu.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China