in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Niyyar Sin na karfafa dangantaka tsakanin kasashe masu arziki da masu tasowa ta samu babban yabo a MDD
2015-09-27 18:22:06 cri
Sanarwar da kasar Sin ta bayar na cewa za ta fi fifita da tallafawa dangantaka tsakanin kasashe masu tasowa ta samu babban yabo a ranar Asabar a yayin dandalin da kasar Sin da MDD suka shirya tare.

"Ina matukar nuna godiya da wannan muhimmiyyar kyauta da wannan niyya taku mai karfi. Wannan wani tunani ne mai cike da haske", in ji sakatare janar na MDD, Ban Ki-moon, dake shugabantar zaman taro na manyan jami'ai kan dangantaka tsakanin kasashe masu tasowa.

Duk a wannan rana, shugaban Sin Xi Jinping ya ba da sanarwa a yayin babban taron MDD kan ci gaba mai karko cewa Sin za ta tattara dalar Amurka biliyan biyu domin bunkasa irin wannan dangantaka.

Takwaransa na kasar Afrika ta Kudu, Jacob Zuma, dake shugabantar gungun 77 a wannan karon, ya nuna godiya sosai ga shugaba Xi game da wadannan shawarwari masu ma'ana da tasiri, a yayin da ita kuma shugabar gwamnatin Bangladesh Sheika Hasina ta kimanta su a matsayin shawarwari masu nagarta.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa wannan dandali yana da muhimmancin gaske. A cewarsa, yana wakiltar wata dama ta yin musanyar ra'ayoyi kan yadda za a karfafa dangantaka tsakanin kasashe masu tasowa bisa tsarin aiwatar da shirin bunkasuwa na bayan shekarar 2015. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China