in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Da alamun jam'iyya mai mulki a Tanzaniya za ta sake lashen zaben shugaban kasar da za a yi
2015-09-23 10:48:41 cri
Wata kuri'ar jin ra'ayin jama'a mai zaman kanta da aka fitar ta nuna cewa, kashi 65 cikin 100 na al'ummar kasar Tanzaniya sun fi kaunar zabar dan takadar shugabancin kasar na jam'iyya mai mulki a zaben shugaban kasar da zai gudana a watan Oktoba.

Sakamakon kuri'ar jin ra'ayin jama'ar da wata kungiya mai rajin tabbatar da adalci ta tattara ya nuna cewa, sama da kashi 62 cikin 100 na 'yan kasar hankalinsu ya fi karkata ga jam'iyyar CCM mai mulkin kasar fiye da dukkan jam'iyyun siyasun kasar.

Sakamakon kuri'ar jin ra'ayin ya kuma nuna cewa, Jam'iyyar adawa ta CHADEMA ce za ta ci gaba da kasancewa ta biyu, inda dan takararta Edward Lowassa ya samu kashi 25 cikin 100 a kuri'ar jin ra'ayin jama'ar da aka tattara.

A ranar 25 ga watan Oktoba ne al'ummar kasar Tanzaniya za su zabi sabon shugaban kasa da 'yan majalisun dokoki. Kuma 'yan takara 8 ne za su fafata a zaben shugaban kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China