in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon jakadan Tanzania a kasar Sin ya bayyana kasar Sin a matsayin amintacciyar kawa ga kasarsa
2014-10-28 10:52:56 cri
Tsohon jakadan Tanzania a nan kasar Sin Charles Sanga, ya bayyana kasar Sin a matsayin wata aminiya ga kasarsa. Cikin wani sharhin da jaridar People's Daily ta kasar Sin ta buga, Sanga ya yi tsokaci kan tarihin dangantakar sada zumunta tsakanin Sin da Tanzania tun daga karni na 15.

Daga nan sai ya yabawa Sin bisa gudummawar da take baiwa kasashen Afirka ba tare da gindaya wani sharadi ba. Baya ga goyon bayanta gare su wajen yaki da mulkin mallaka, da samun bunkasuwar tattalin arziki. Kana ya ce, kasar Sin ta kiyaye sada zumunta tsakaninta da kasashen Afirka, yayin da take samun babbar nasara kan bunkasuwar tattalin arziki da dagawar matsayinta a duniya. A ganinsa, wannan zumunta na wanzuwa bisa tushen girmama juna da cimma moriyar juna.

A daya hannun, Mr. Sanga ya bayyana gagarumin ci gaban da kasar Sin ta samu sakamakon aiwatar da manufar bude kofa da yin kwaskwarima a matsayin sabuwar dama ga kasashen Afirka, kana ya bayyana cewa idan har kasashen Afirka na son samun bunkasuwa, to kamata ya yi su kara koyi daga fasahohi daga kasar Sin ke bi.

Kaza lika ya yi imani da cewa, a matsayin amintacciyar abokiyar kasashen Afirka, kasar Sin za ta iya taimakawa kasashen na Afirka wajen samun 'yancin kai a fannin siyasa, da samun bunkasuwar tattalin arziki na kashin kan su. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China