in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan karfafa yin hadin gwiwa tare da kasashen Afirka
2015-09-21 21:07:37 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin, Hong Lei ya shaidawa taron manema labaru a yau cewa, Sin na fatan inganta yin hadin gwiwa a fannonin gina hanyoyin jirgin kasa na zamani da na motoci da jirgin sama, da raya masana'antu, da samar da makamashi tare da kasashen Afirka.

A jiya ne, a birnin Addis Ababa na kasar Habasha aka kaddamar da hanyar jirgin kasa da kamfanin gina layin dogo na kasar Sin ya gina.

Game da wannan batu, Hong Lei ya ce, yanzu kasashen Afirka suna kara kokarin raya masana'antunsu, haka kuma suna bukatar gaggauta raya manyan ababen more rayuwarsu..

A matsayinta na aminiyar kasashen Afirka, Sin za ta sa kaimi ga yin hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a wadannan fannoni, a kokarin inganta samun ci gaba tare tsakanin Sin da kasashen Afirka, da kuma kawo alheri ga jama'arsu baki daya.

Rahotanni na cewa, wannan ita ce hanyar jirgin kasa mai amfani da wutar lantarki ta farko a kasar Habasha, har ma da nahiyar Afirka dake kudu da Sahara, wadda za ta magance matsalar zirga-zirga da ake fuskanta a hedkwatar kasar.(fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China