in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tsohon shugaban kasar Namibia yana fatan kasarsa za ta zurfafa mu'amala a fannonin tattalin arziki da cinikayya da Sin
2015-08-27 10:36:35 cri
Tsohon shugaban kasar Namibia Hifikepunye Pohamba ya bayyana a jiya cewa, yana son kasarsa ta kara yin mu'amala da Sin a fannonin tattalin arziki da cinikayya da sa kaimi ga samun moriyar juna.

Hifikepunye Pohamba ya bayyana hakan ne yayin da ya halarci taron dandalin tattaunawa karo na 4 tsakanin jama'ar kasar Sin da kasashen Afrika a birnin Yiwu dake lardin Zhejiang na kasar Sin.

Bayan taron, ya bayyana wa wakilinmu cewa, yana fatan kasashen biyu za su inganta hadin gwiwar cinikayya a tsakanin su, kuma jama'ar kasashen Afirka suna son ganin an kara shigar da kayayyakin Sin zuwa kasashensu tare da samun saukin zaman rayuwa

Hakazalika, Pohamba yana son Sin da kawacen harajin kwastam na kudancin Afirka za su kafa yankin ciniki cikin 'yanci don sa kaimi ga samun bunkasuwar Sin da kudancin Afirka. Kana za a taimakawa daukacin kasashen Afirka bisa tsarin hadin gwiwar kungiyar AU. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China