in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar tsaron shugaban kasar Burkina Faso ta sako shugaban wucin gadi
2015-09-19 13:51:03 cri
Majalissar wanzar da dimokaradiyyar kasar Burkina Faso wadda rundunar tsaron shugaban kasar ta kafa a matsayin hukumar kolin kasar, ta sanar da sako shugaban wucin gadin kasar Michel Kafando, tare da wasu ministoci guda biyu da rundunar ta tsare. Sai dai sanarwar ba ta bayyana ko an sako firaministan wucin gadin kasar Isaac Zida ba. Har wa yau, majalissar wanzar da dimokaradiyyar ta ce an sake bude kan iyakar kasar a jiya Jumma'a.

A wani ci gaban kuma, shugaban karba-karba na kungiyar tarayyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ta (ECOWAS), kuma shugaban kasar Senegal Macky Sall, tare da shugaban kasar Benin Boni Yayi sun tashi zuwa birnin Ougadougou, domin fara aikin shiga tsakani, game da rikicin kasar ta Burkina Faso.

A ranar Larabar da ta gabata ne rundunar tsaron shugaban kasar Burkina Faso dake biyayya ga tsohon shugaban kasar, ta cafke shugaba da firaministan wucin gadin kasar, tare da wasu ministoci biyu na gwamnatin. A kuma ranar Alhamis rundunar ta sanar da karbe madafan ikon kasar, tare da hambarar da shugaban wucin gadin kasar, tare da rushe gwamnatin wucin gadin.

Har wa yau, rundunar ta kuma sanar da kafa majalissar wanzar da dimokaradiyyar kasar a matsayin hukumar kolin kasar. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China