in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamaru : Wani harin kunar bakin wake ya hakala mutane biyar a ranar Lahadi
2015-09-21 10:06:56 cri
A kalla mutane biyar suka mutu, wanda ya hada da dan sanda guda, a yayin da aka kai wani harin kunar bakin wake a wata tashar tsaro dake kunshe da jami'an tsaro na 'yan sanda, garda sarki da kuma sojoji, a ranar Lahadi da safe a yankin arewa mai nisa na kasar Kamaru, a cewar wasu majiyoyin soja.

Harin da ake ganin akwai hannun kungiyar Boko Haram, ya faru ne a Mora, wani yankin dake iyaka da Najeriya, mai tazarar kilomita 80 daga Maroua, muhimmin birnin dake kuriyar arewacin kasar Kamaru. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China