in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai harin bam har sau biyu da ya jawo mutuwar mutane 15 a arewacin Kamaru
2015-09-04 13:03:20 cri
Rahotanni daga Younde babban birnin kasar Kamaru ya tabbatar da cewar a kalla mutane 15 ne suka rasa rayukansu, wassu da dama kuma suka jikkata lokacin wani harin bam guda biyu a arewacin kasar.

Bam din farko dai an ce ya fashe ne a tsakiyar kasuwa a garin Kerawa wanda yake kan iyaka da kasar Nigeriya sannan bam na biyu ya fashe a kusa da wani sansanin soji inda a nan ne mutane 15 suka mutu kamar yadda wata majiyar tsaro ta tabbatar.

Wadanda suka mutu dai a kasuwa har yanzu ba'a samu adadin su ba, in ji majiyar da ta nemi a sakaya sunanta.

Kasar Kamaru dai ta shiga cikin jerin kasashe na hadin kan yankuna na Afrika da ke yaki da kungiyar 'yan Boko Haram na Nigeriya. Garin Kerawa dai yana da nisa daga arewacin kasar, kuma ya fuskanci gwagwarmaya tsakanin sojin kasar da na 'yan kungiyar Boko Haram. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China