in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi: shugaban kasar Sin zai kai ziyara Amurka don inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu da kuma kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya
2015-09-18 11:17:30 cri

Jaridar People's Daily ta kasar Sin ta wallafa wani sharhi da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya rubuta mai taken "inganta hadin gwiwa a tsakanin Sin da Amurka, da kuma kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya". Sharhin na cewa, ziyarar da shugaba Xi Jinping zai kai kasar Amurka tare da halartar tarurukan MDD za su taimaka wajen inganta raya hadin gwiwa a tsakanin Sin da Amurka, da kuma kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya, ta yadda za a samar da kyakkyawar makoma ta dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma inganta rayuwar dan Adam.

Sharhin ya kara da cewa, wannan ne karo na farko da shugaba Xi Jinping ya kai ziyarar aiki kasar Amurka tare da kai ziyara a hedkwatar MDD. Zai kai ziyarar ce a daidai lokacin cika shekaru 70 da yaki da masu ra'ayin nuna karfi a duniya da kuma kafuwar MDD, don haka ziyarar tana da matukar muhimmanci. Babu shakka wannan ziyara za ta kasance wata muhimmiyar ziyara yayin da ake raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka da kiyaye zaman lafiya da samun bunkasuwa a duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China