in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci babban sakataren hukumar FIFA ya yi murabus
2015-09-18 09:50:04 cri
Hukumar wasan kwallon kafa ta duniya wato FIFA, ta fidda wata sanarwa a daren jiya Alhamis a birnin Zurich, wadda ke cewa tuni aka bukaci babban sakataren hukumar Jérôme Valcke da yin murabus.

Sanarwar ta bayyana cewa, hukumar FIFA ta gano wasu zarge-zarge da aka yiwa Valcke, kana ta bukaci kwamitinta na kula da da'ar ma'aikata da ya gudanar da bincike a kan sa.

Jérôme Valcke mai shekaru 54 da haihuwa, ya zama babban sakataren hukumar FIFA a shekarar 2007. Yayin da ake bincike kan laifuffukan cin hanci a hukumar ta FIFA, an zarge shi da fidda kudi har dala miliyan 10 daga kasar Afirka ta Kudu, zuwa aljihun Jack Warner a shekarar 2008, wanda a lokacin ke kan kujerar shugaban hukumar wasan kwallon kafa ta yankin Arewacin Amurka da ta tsakiya, da yankin Caribbean .

A ganin hukumar shari'a ta kasar Amurka, fidda wadannan kudi a matsayin toshiyar baki, yana da nasaba da neman baiwa kasar Afirka ta Kudun damar karbar bakuncin gasar cin kofin duniya da ya gabata a shekarar 2010. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China