in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Matakan soji da kasashen yamma suka dauka ne ya haddasa matsalar 'yan gudun hijira, in ji kafofin kasar Italiya
2015-09-14 15:17:45 cri
A gabar da ake fuskantar tsanantar matsalar 'yan gudun hijira a nahiyar Turai, wasu manyan jami'an kasar Italiya, da manema labarun kasar, sun bayyana cewa, matsalar ta abku ne sakamakon shisshigin da kasashen yammacin duniya suka yi na daukar matakan soji a wasu kasashen yammacin Asiya da na arewacin Afirka, don haka a halin da ake ciki kasashen na Turai suna girbar abin da suka shuka ne a baya, bisa aiwatar da manufofin da aka tsara ba tare da nuna hangen nesa ba.

Cikin wasikar da Matteo RENZI, firaministan kasar Italiya ya rubutawa manyan kafofin watsa labarai na kasashen Turai a kwanakin baya, ya ce kasashen yamma sun kasa hangen mummunan tasirin da shirye-shiryen da suka tsarawa kasashen Libya, da Syria za su haifar a gaba, haka kuma sun yi kuskure wajen ganin kansu a matsayin masu karfin kafa sabbin hukumomi a kasashen 2.

Shi kuwa tsohon ministan harkokin wajen kasar Italiya, Franco Frattini, cewa ya yi rashin hangen nesa ne ya sa kasashen yammacin duniya suka aikata babban laifi a kasar ta Libya, inda janyewar sojojinsu ta haifar wa kasar tsunduma cikin babbar matsala. Zuwa yanzu dakarun kasar Libya suna kokarin hada baki da masu tsattsauran ra'ayi na kungiyar IS, lamarin da ya haddasa yakin basasa a kasar, gami da barazanar tsaro ga kasashen Turai.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China