in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yadda ake samun gurbataccen hazo a kasashen Turai na nuni ga kalubalen dake tare da magance matsalar
2015-03-23 10:58:08 cri
A makon da ya gabata, birnin Londan ya murtuke da gurbataccen hazo, wannan yanayi ya kuma shafi birnin Paris na kasar Faransa, gami da sauran wurare daban daban dake nahiyar Turai, wanda hakan ya sanya jama'ar kasashen Turai damuwa game da lafiyar jikinsu.

A daya hannun kuma hakan ya sanya gurbataccen hazon, wanda ake samu sakamakon yawan fitar da hayaki mai gurbata muhalli, ya sake zamowa wani batun dake janyo hankalin jama'ar kasashen duniya.

Yadda gurbataccen hazo ya far wa kasashen Turai, ya tunasar da cewa, aikin daidaita matsalar samun gurbataccen hazo, wani aiki ne mai matukar wuya, wanda zai dauki lokaci mai tsawo kafin a cimma nasarar sa. Kaza lika kasashen Turai sun fara kayyade fitar da gurbatacciyar iska a farkon shekarun 1970, matakin da ya hada da kara inganta makamashi. Wadannan matakai sun yi amfani, amma ba a cimma nasarar kau da matsalar fitar da gurbatacciyar iska a kasashen Turai gaba daya ba tukuna. Yadda a wannan karo aka sake samun gurbataccen hazo a kasashen Turai ya nuna cewa, matsalar gurbataccen hazo ba a wata kasa ko wani yanki kadai ta takaita ba, wato matsalar da ta shafi dukkanin kasashe, tana kuma bukatar hadin gwiwar dukkanin kasashen duniya wajen warware ta. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China