in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude rumfunan zaben raba gardama kan batun yarjejeniyar bashin kasar Girka
2015-07-05 17:34:32 cri
Yau Lahadi 5 ga wata, ana gudanar da zaben raba gardama kan batun yarjejeniyar bashin kasar Girka, lamarin zai haifar da babban tasiri kan yadda za a iya warware rikicin bashin kasar Girka da kuma matsayin kasar a kungiyar tarayyar Turai, kuma ana tsammanin samun sakamakon wannan zaben a yau da dare.

Tun karfe bakwai da safe har zuwa karfe 7 da dare a yau, za'a ci gaba da gudanar da zaben a kasar ta Girka, kuma bisa kididdigar da hukuma mai kula da harkokin cikin gida ta kasar Girka ta yi, an ce, adadin jama'ar kasa dake da ikon kada kuri'u ya kai kimanin miliyan 9 da dubu 800, haka kuma shirya zaben cikin gajeren lokaci, ya sa, 'yan kasar Girka dake ketare ba za su samu damar kada kuri'u kan zaben raba gardamar ba.

Bisa dokokin kasar, sai a kalla adadin masu kada kuri'u ya kai kashi 40 bisa dari, sannan sakamakon zaben zai yi tasiri ga makomar kasar.

Haka kuma, bisa binciken da aka yi dangane da jin ra'ayin jama'ar kasar Girka, an ce, adadin masu amincewa da na masu rashin amincewa na kunnen doki, shi ya sa, ba za a iya yin wani hasashe kan sakamakon zaben din ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China