in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sarkin Saudi Arabiyya ya bukaci a gudanar da bincike yadda ya kamata kan hadarin fadowar karfen daukan kaya
2015-09-13 14:08:19 cri

A daren ranar 12 ga wata, sarkin Saudi Arabiyya Salman bin Abdulaziz Al Saud ya ziyarci wurin da karfen daukan kaya a masallacin Harami ya fado, inda ya bukaci bangarorin da abin ya shafa da su gudanar da bincike kan dalilin aubkuwar hadari daga dukkan fannoni, domin samar da bayani ga jama'a yadda ya kamata.

A ran 11 ga wata, wani karfen daukan kaya mai girma ya fado ba zato ba tsammani a masallacin Harami, wanda ya haddasa rasuwar mutane 107, yayin da sama da 200 suka jikkata, haka kuma, galibin dake cikin wadanda suka rasa rayukansu, su ne musulman da suka zo daga kasashen Indonesia da kuma India.

A halin yanzu, bangarorin da abin ya shafa na kasar Saudi Arabiyya sun fara gyara wurin da hadarin ya auku, da kuma fara gyara masallacin a wuraren da suka lalace sakamakon hadarin, domin sake karbar masu aikin hajji da sauri. Kana, hukumar addini ta kasar Saudi Arabiyya ta bayyana cewa, za a ci gaba da gudanar da ayyukan hajji na shekarar bana bisa lokacin da aka tsara, watau a ran 21 ga watan da muke ciki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China