in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon harin da aka kai a wani masallaci a Pakistan sun karu
2015-01-31 17:13:47 cri

Kafofin yada labaru a kasar Pakistan, sun ce yawan mutanen da suka rasu sakamakon harin bam da aka kai kan wani masallaci a jiya Jumma'a sun kai mutane 54, baya ga wasu fiye da 50 da suka samu raunuka.

Rahotanni dai sun bayyana cewa an kai harin ne kan wani masallacin 'yan Shi'a dake yankin Shikarpur dake lardin Sindh dake kudancin kasar.

'Yan sanda sun ce mutane da dama sun rasu sakamakon rufzawar da masallacin ya yi a kansu. Sun ce bam din ya tashi lokacin da kimanin mutane 600 ke salla cikin masallacin.

Bayanai na cewa mai iyuwa ne adadin mutane da harin ya hallaka ya ci gaba da karuwa, sakamakon matsanancin hali da wasu wadanda harin ya ritsa da su ke ciki yanzu haka.

Kawo yanzu dai gwamnatin kasar ba ta ce komai game da harin ba tukuna, sai dai kafofin watsa labaran yankin sun labarta cewa, wata kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta 'yan Sunni mai suna Jundallah, ta sanar da daukar alhakin kai harin, kungiyar da tun bara ta bayyana mubaya'ar ta ga kungiyar IS mai da'awar kafa daular Islama. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China