in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya ta baiwa jihar Diffa ta kasar Nijar taimakon abinci
2015-03-01 15:43:09 cri
Ministar harkokin wajen kasar Nijar, madam Kane Aichatou Boulama, ta karbi a ranar Asabar da wani muhimmin taimakon abinci daga gwamnatin kasar Aljeriya ta hannun wakilin ma'aikatar harkokin waje, dake kula da harkokin Afrika da yankin Magreb, mista Aldoul Kader Messahel. Taimakon na ton 240, da suke hada da shinkafa, madara, garin hanci, suga, man girki, da sabulu da sauransu, zai je zuwa taimakawa al'ummomin jihar Diffa dake fama da mawuyacin hali sakamakon hare haren kungiyar Boko Haram.

Da take karbar wannan taimako, ministar harkokin wajen Nijar madam Aichatou Boulama ta tunatar da cewa kasar Aljeriya 'yar uwa ce ga kasar Nijar a ko da yaushe take a shirye domin amsa kiran gwamnatin Nijar domin taimakawa al'ummomin jihar Diffa.

Haka kuma, ministar ta nuna godiya ga gwamnatin Aljeriya bisa wannan tallafi, musamman ma zuwa wakilin minista dake kula da harkokin Afrika da yankin Magreb wanda ya zo da kansa domin isar da wannan taimakon kasarsa zuwa ga kasar Nijar a cikin shirin gaggawa game da jihar Diffa.

A nasa bangare a yayin da yake mika wannan taimako, ministan Aljeriya, ya mika yabo na musammun ga gwamnati da al'ummar kasar Nijar kan yadda suka karbi mutanen Nijeriya da ba su mafaka a kasar Nijar.

Mista Abdoul Kader Messahel ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da masu hannu da shuni da su ba da nasu taimako, domin taimakawa kokarin gwamnatin Nijar wajen kai dauki ga al'ummomin dake jihar Diffa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China