in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gabatar da takardar bayani game da batun raya yankin Tibet na kasar Sin
2015-04-15 15:45:17 cri
Ofishin watsa labaru na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gabatar da takardar bayani game da zabin hanyarmai taken " Hanyar da aka zaba wajen raya yankin Tibet " a yau Laraba 15 ga wata, inda aka yi bayani game da nasarorin da aka samu yayin da ake raya yankin Tibet, da bayyana nuna ra'ayin cewa hanyar raya yankin Tibet shi neita ce wani muhimmin zabi a cikin tarihin yankin Tibet.

Takardar ta bayyana cewa, yankin Tibet kashi daya ne na kasar Sin, kuma kabilar Tibet tana daya daga cikin kabilun kasar Sin. Yankin Tibet ya dauki wannan hanyar raya yankin ta yanzu, wanda wadda ta dace da bunkasuwar al'adu da zamani, da zamantakewar al'ummar dan Adam, da halin da ake ciki a kasar Sin, da kuma moriyar jama'ar yankin Tibet daga 'yan kabilu daban daban.

Hakazalika kuma, takardar ta yi nuni da cewa, yankin Tibet ba zai samu kyakkyawar makoma ba sai dai idan an tsaya tsayin daka kan hadin kai, da kokarin neman samun ci gaba da zaman lafiya, da kuma yaki da ayyukan ra'ayin barakaaware da koma baya da kuma rikice-rikice. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China