in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata Afrika ta rika sarrafa albarkatun ma'adinanta da kanta in ji shugaban Afrika ta Kudu
2015-06-13 13:18:33 cri
Shugaban kasar Afrika ta Kudu Jacob Zuma ya nuna a ranar Jumma'a cewa abu mai muhimmanci ga nahiyar Afrika shi ne na sarrafa albarkatun ma'adinanta a nahiyar.

Wannan dalilin ya sa muka dauki niyya, a matsayinmu shugabanni, cewa bai kamata mu ci gaba da sarrafa albarkatun ma'adinanmu a wajen nahiyar Afrika ba, dukkan albarkatunmu ya kamata a ce ana sarrafa su a nan Afrika ta yadda al'ummomin kasashen Afrika za su samu moriya, in ji shugaba Zuma a yayin taron kungiyar Afrika karo na 25 da ke gudana a birnin Jonhannesburg.

Zuma ya yi wannan kira a yayin da yake halartar wani taron "babban aiki na shugabancin kungiyar AU" wanda burinsa shi ne tattara kudade domin gidauniyyar tarayyar Afrika.

Zuma ya karbi bakuncin dukkan shugabanni da gwamnatoci har ma da tawagogi daban daban a wannan dandali na tarihi, tare da bayyana cewa Afrika ta Kudu, na farin ciki da karramawar da aka mata na karbar jagoranci na nahiyarmu domin wannan muhimmin dandali.

Dandalin na gudana a cibiyar yarjejeniyar kasa da kasa ta Sandton da ke birnin Johannesburg bisa taken: Shekarar wayin kan mata da bunkasuwa game da ajandar shekarar 2063 na Afrika". (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China