in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasa da kasa za su halarci taron koli na raya MDD
2015-09-04 13:23:54 cri
Ofishin watsa labaran MDD ya fidda bayanin cewa, shugabanni na kasashen duniya sama da dari za su halarci taron raya MDD da za a yi tun ranar 25 zuwa ranar 27 ga watan Satumba. Haka kuma, a yayin taron, za a zartas da jadawali na samun dauwamammen ci gaba na MDD bayan shekarar 2015, inda zai kunshi buri guda 17, domin tsara hanyoyin neman bunkasuwa kan hadin gwiwa da ci gaban kasa da kasa cikin shekaru 15 masu zuwa.

Kana, a cikin rahoton da aka fidda, an ce, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon na ganin cewa, taron koli zai bude wani sabon shafi wajen neman dauwamammen ci gaban duniya, a lokacin, za a kawar da talauci, samun bunkasuwa da nishadi, da kuma warware matsalar sauyin yanayi yadda ya kamata.

Bugu da kari, an ce, za a yi cikakken zaman taron shugabannin kasa da kasa a yayin da ake gudanar da taron kolin, da kuma yin shawarwari kan yadda za a iya kawar da talauci, baiwa mata iko, warware matsalar sauyin yanayi da dai sauran harkokin da ya shafi neman dauwamammen ci gaba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China