in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon na yin kira da a kawar da makaman nukiliya a duniya
2015-08-30 13:57:19 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga kasashen duniya da ba su zartas da yarjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya daga dukkan fannoni da su hanzarta zartas da yerjejeniyar domin kawar da makaman nukiliya daga doron duniya.

Mr Ban ya yi wannan kiran ne yayin da ya ke jawabi a ranar hana gwajin makaman nukiliya ta duniya wato 29 ga watan Agustan kowa ce shekara

Ban Ki-moon ya ce, shekaru 70 da suka gabata ne aka fara gwajin makaman nukiliya a duniya, kuma hanyar da ta fi dacewa a tuna da wadanda aka yi musu laifi ita ce a daina irin wannan gwaji a nan gaba. Ya ce, yarjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya daga dukkan fannoni da aka zartas da ita a shekarar 1996 tana da muhimmiyar ma'ana wajen kawar da makaman nukiliya.

Kuma tun bayan shekaru 20 da suka wuce, har yanzu ba a iya fara yin amfani da yarjejeniyar ba sabo da wasu kasashen duniya ba su sa hannu kan ita ba.

Bugu da kari, Ban Ki-moon ya ce, ana maraba da kasashen dake da makaman nukiliya da su dakatar da gwajin nukiliya, a sa'i daya kuma, ya bukaci daukacin kasashen duniya da su sanya hannu da kuma zartas da yarjejeniyar hana gwajin makaman nukiliya daga dukkan fannoni. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China