in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin kasa da kasa sun gaggauta shirya yaki da kungiyar Boko Haram
2015-08-24 10:26:15 cri
An rufe taron hafsoshin sojojin hadin gwiwa na kasashe 5 da ke yankin tebkin Chadi a ranar Asabar a birnin N'Djamena na kasar Chadi, inda aka tattauna matakan da sojojin kasashen za su dauka wajen gaggauta yaki da kungiyar Boko Haram.

Rahotanni na nuna cewa, yayin taron an tattauna batutuwan dake shafar yankunan da aka tura sojojin, yawan sojojin da aka jibge, ka'idojin gudanar da ayyuka, jadawalin ayyukan da za su gudanar, yawan kudin da za a kashe yayin da ake gudanar da ayyuka da dai sauransu. An tabbatar da cewa, yawan sojojin hadin gwiwar ya kai 8700, kuma za a raba su ne a rukunoni 5, inda za a jibge su a yankuna 3 na yakin. Kana an kafa hedkwatar da ke kula da rundunar sojojin a birnin N'Djamena na kasar Chadi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China