in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta tabbatar da karshen Ebola a kasar Liberiya
2015-09-03 19:49:58 cri
Hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO a ranar Alhamis din nan ta tabbatar da karshen cutar Ebola a kasar Liberiya. A cikin wani sanarwar da ta fitar, ta ce hakan ya biyo bayan kokarin da Liberiya ta yi na daukan mataki yadda ya kamata ta hanyar sa ido da daukan matakan gaggawa da kuma hadin gwiwwa da sauran kasashen waje. Yanzu haka Liberiya ta shiga kwanaki 90 na matsayin koli da ake kaiwa na sa ido.

A Liberiya an sanar da karshen yaduwar cutar ne tun a ranar 9 ga watan Mayu amma kuma sai cutar ta sake bulla a ranar 29 ga watan Yuni inda aka samu wassu masu dauke da ita su 6.

A karkashin bincike da sa ido da ake yi gwamnatin Liberiya cikin sauri ta dauki matakin dakile sabon bullowar cutar. Hukumar ta WHO ta jinjina ma gwamnatin kasar tare da al'ummar ta bisa ga wannan nasara tana mai tabbatar da cewa za ta ba da dukkan taimakon da ya wajaba a cikin kwanaki 90 na matakin koli na binciken cutar da kuma kokarin ganin saurin farfadowar kasar. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China