in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata mata ta kamu da cutar Ebola a kasar Saliyo
2015-09-01 10:35:16 cri
A karshen makon da ya wuce ne aka tabbatar da harbuwar wata mata da cutar Ebola bayan da ta rasu, kwanaki 42 kafin a cikar wa'adin kawar da cutar daga Saliyo, duk kuwa da cewa a yanzu haka kasar ta shafe kwanaki 6 ba tare da samun sabbin wadanda suka kamu da cutar ba.

A jiya Litinin ne dai wani jami'in watsa labaru a cibiyar lura da cutar Ebola dake kasar ta Saliyo Yaya Tunis, ya bayyanawa majiyar mu cewa, an tabbatar wannan mata yar shekaru 60 a duniya ta kamu da cutar Ebola ne bayan ta rasu kafin a yi mata jana'iza. Kafin hakan an shafe kwanaki 50 ba a gano sabbin masu kamuwa da cutar ba a yankin Kambia inda matar take da zama.

Jami'in ya kara da cewa, an riga an kebe mutane 10 da suka yi cudanya da wannan mata, kana kungiyoyi biyu na gwamnatin kasar sun soma bincike kan asalin cutar, ba kuma da jimawa ba za a tsaida kuduri kan ko za a killace dukkanin al'ummar da wannan mata ke zaune da su ko a'a. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China