in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta rage adadin sojinta nan da shekarar 2017
2015-09-03 16:51:11 cri
A ranar Alhamis din nan Kasar Sin ta ce za ta kamala rage adadin sojinta da kusan 300,000 nan da karshen shekarar 2017, a wani kokari na yanzu da take yi wajen samar da rundunar soji kadan amma masu karfi.

Wannan sanarwa ta fito ne daga bakin kakakin ma'aikatar tsaron kasar, Yang Yujun bayan da Shugaban kasar Xi Jinping ya yi alkawarin rage adadin sojin a lokacin gagarumin faretin sojin cika shekaru 70 na kawo karshen yakin duniya na biyu da aka yi a safiyar yau din a dandalin Tian'anmen dake birnin Beijing.

Yang ya ce wannan yunkurin musamman zai mai da hankali a kan rundunar da suke da tsaffin kayayyakin aikin soja, ma'aikatan bangaren mulki da kuma ma'aikatan da ba su aikin soji domin gyara tsarin rundunar kasar.

Ya ce rage adadin ya biyu bayan tsarin da ake da shi a yanzu na sojin kasa da halin da ake ciki a kasar. Ya kara da cewa adadin rundunar zai ragu amma kuma zai yi takara da saura kuma tsarinsu za su fi mai da hankali a kimiyya.

Wannan ne zai zama karo na hudu da kasar ta rage adadin rundunarta tun daga shekara ta 1980 wanda a lokacin take da yawan soji a duk fadin duniya na miliyan 2.3. A shekara ta 1985 kuma ta sake rage adadin da kusan miliyan 1 mafi girma a ragewa da kasar ta fuskanta. Yang Yujun ya yi bayanin cewa wannan kwaskwarima zai bi tsarin mataki mataki ne, a hankali za'a ci gaba da fitar da wassu matakan. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China