in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen Sin ya gana da takwaransa na Iran
2015-07-03 10:18:26 cri

A jiya Alhamis ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Iran Javad Zarif a yayin da suke halartar shawarwari kan batun nukiliyar Iran, wanda ya gudana a birnin Vienna, inda bangarorin biyu suka tattauna sosai kan batutuwan da suka shafi yadda ake gudanar da shawarwarin, da kuma matsalolin da ake fuskanta a yanzu.

A yayin ganawar Wang Yi ya bayyana cewa, shawarwarin da aka dade ana yi ya shiga wani muhimmin mataki na karshe, saboda haka nauyin a bisa wuyan bangarori daban daban da abin ya shafa shi ne su yi kokarin cimma wata yarjejeniyar da ta shafi dukkan fannoni. Wang ya ce, kasar Sin na fatan bangarorin za su iya kawar da duk wani cikas domin cimma yarjejeniya mai adalci da daidaici. Kasar Sin ma na son ci gaba da taka rawarta a wanan fannin.

A nasa bangaren Javad Zarif ya bayyana cewa, kasar Iran ta yaba sosai ga taimakon da kasar Sin ta bayar wajen inganta shawarwari game da batun nukiliyar Iran, tare da fatan Sin za ta dauki matsayi mai adalci domin ci gaba da taka muhimmiyar rawa kan wannan batun. Ya kara da cewa, kasarsa na kokarin ganin an cimma wata yarjejeniya a dukkan fannoni, tare da cire takunkumin da aka saka mata, tana kuma son yin mu'ammala sosai tare da Sin a wannan fanni. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China