in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin jiragen sama na Sin ya bude hanya ta farko zuwa nahiyar Afirka kai tsaye
2015-08-05 10:59:07 cri
Kamfanin jiragen sama na Southern Airlines na kasar Sin, ya kaddamar da hanyar jiragen sama tsakanin birnin Guangzhou na kasar Sin zuwa birnin Nairobi na kasar Kenya a Larabar nan 5 ga watan Agusta. Wannan ce dai hanyar sufuri ta farko da wani kamfanin jiragen saman Sin ya bude zuwa kasar Kenya kai tsaye, kana ita ce hanya daya tak ta jiragen sama da Sin ta hada da nahiyar Afirka a halin yanzu.

Bude wannan hanya muhimmin mataki ne da kamfanin na Southern Airlines na kasar Sin ya dauka, domin kara hadin gwiwar harkar zirga-zirgar jiragen sama a yankin, da bin manufofin "Ziri daya da hanya daya" na kasar Sin, da kuma biyan bukatu na mu'amala a tsakanin jama'ar Sin da Kenya.

A shekarun baya baya nan, ana samun bunkasuwa cikin sauri a fannin mu'amalar tattalin arziki da cinikayya da al'adu a tsakanin Sin da Afirka. Kuma yawan fasinjojin dake hawa jiragen sama a tsakanin Sin da Afirka na karuwa da kashi 15 cikin dari a kowace shekara, adadin da ya kai miliyan 1 da dubu 500 kan shekara guda.

Kaza lika Sin ta daddale yarjejeniyar hadin gwiwa a fannin jigilar da kaya a tsakaninta da kasashen Afirka 17, kamarsu Habasha, da Afirka ta Kudu, kuma ta sa hannu kan daftarin yarjejeniya a wannan fanni tare da kasashen Afirka 6 ciki hadda Seychelles.

Jiragen sama masu lamba CZ633/634 na kamfanin Southern Airlines na kasar Sin, za su rika tashi sau uku a ko wane mako zuwa birnin Nairobi daga birnin Guangzhou, tafiyar da tsayin ta ya kai sa'oi 11. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China