in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a kara yada rubuce-rubucen kasar Sin a Afirka ta Kudu
2015-08-06 10:19:54 cri
Madaba'ar kasar Sin ta CIPG, ta sha alwashin yada karin littattafai game da kasar Sin a Afirka ta Kudu, domin baiwa 'yan kasar damar fahimtar Sin.

Babban daraktan madaba'ar Li Jianguo ne ya bayyana hakan, ya yin zantawar sa da wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua. Ya ce baya ga littattafai, za su samar da mujallu da shafukan yanar gizo, domin samar da karin bayanai game da kasar Sin.

Mr. Li ya kara da cewa sun samu matukar kwarin gwiwa daga masu karatu, a yayin bikin baje kolin littattafai da suka halarta a birnin Johannesburg, tsakanin ranekun 31 ga watan Yuli zuwa 2 ga watan nan na Agusta.

Ya ce a matakin farko madaba'arsa za ta samar da littattafai game da tarihin kasar Sin, da yarukan ta, da rubuce-rubucen bincike, da na sassan ilimi, da ci gaban al'adu da tattalin arziki. A cewar sa za su yada wadannan littattafai ne kasancewar Sin kasa ce da a yanzu ke kara yin fice a idon duniya.

Kaza lika jagoran na CIPG ya ce kyakkyawar dangantakar dake tsakanin Afirka ta kudu da Sin, ta sanya mutane da dama maida hankali ga neman sanin tarihi da yarukan kasar Sin.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China