in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin kasar Sin ya rattaba hannu na gina kamfanonin siminti a Afrika.
2015-08-27 09:35:38 cri
Wani kamfanin kasar Sin ya rattaba hannu a kan kwangila ta dalar Amurka biliyan 1.487 tare da rukunin kamfanonin Dangote a kasashen Afrika da dama.

Kamfanonin da Sinoma international engineering na Sin zai gina za'a yi su ne a kasashen da suka hada da Ghana, Habasha, Kwaddibuwa, Kamaru, Mali, Niger, Senegal, Zambiya da kuma Kenya.

Ana sa ran wadannan za su kara adadin metric tan miliyan 25 a wanda yanzu haka kamfanin Dangoten ke samarwa na kusan metric tan miliyan 50.

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote wanda alkalumma suka nuna shi ne mafi arziki a Nahiyar Afrika, Alhaji Aliko Dangote ya shaida ma manema labarai a birnin Ikko na Nigeriya a lokacin rattaba hannun ranar laraban nan cewa ana sa ran aikin gina kamfanonin samar da simintin za'a kamala su ne a cikin watanni 30 a kuma yi bikin bude su a kasar Kamaru.

Alhaji Aliko Dangote ya ce wannan aiki wani ci gaba ne da aka samu a shirin da kamfanin yake yi na kara yawan simitin da yake samarwa zuwa metrik tan miliyan 100 nan da shekara ta 2020. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China