in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira ga Sudan ta Kudu da ta goyi bayan aikin jin kai
2015-07-14 10:32:13 cri
Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi kira ga mahukuntan Sudan ta Kudu da su taimakawa tawagar MDD da masu aikin jin kai da ke kasar, ta yadda za su samu saukin taimakawa mutanen da rikicin kasar ya shafa.

A yayin taron manema labaru na hadin gwiwa da aka shirya a gun taron kasa da kasa kan tattara kudade don samun ci gaba da aka yi a birnin Addis Ababa da shugabar hukumar zartarwar kungiyar AU Nkosazana Dlamini-Zuma, Mr Ban ya ce, tawagar musamman ta MDD da ke kasar Sudan ta Kudu na taimakawa wadanda suka bar gidajensu da dama sakamakon rikicin da kasar ke fama da shi.

Don haka ya yi kira da a baiwa tawagar da masu aikin jin kai damar isar da kayan agaji ga mutanen da rikicin ya shafa.

A yayin da ake bayani game da yunkurin warware rikicin, Madam Nkosazana Dlamini-Zuma ta ce, kungiyar IGAD, da AU da sauran bangarorin da abun ya shafa na kokarin taimakawa bangarorin da ke fada da juna na ganin an kawo karshen yakin da ake yi a kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China