in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala tattaunawa akan Sudan ta kudu ba tare da cimma matsaya ba.
2015-08-18 10:13:42 cri
Tattaunawa akan samar da zaman lafiya a kasar Sudan ta kudu ya kai karshe ba tare da cimma matsaya ba a tsakanin dukkan bangarorin masu fada da juna a ranar litinin din nan.

Kamar yadda masu shiga tsakani na kungiyar raya gwamnatocin kasahen gabashin Afrika IGAD , gwamnatin Sudan ta kudu na bukatar makonni 2 kafin ta rattaba hannu a kan yarjejeniyar zaman lafiyar da bangaren adawa na kasar suka amince da shi.

A karkashin shiga tsakani na kungiyar IGAD , wakilan bangaren adawa da na tsaffin wadanda aka tsare a kasar wato SPLM/SPLA da ma sauran masu ruwa da tsaki sun rattaba hannu akan yarjejeniyar don ganin an cimma karshen wannan takaddama na watanni 20 a jaririyar kasar na duniya.

Wakilan gwamnati karkashin jagorancin Shugaban kasar ta Sudan ta kudu Salva Kiir Mayardit za su tattauna da mazabunsu sannan su dawo bayan makonni 2 don karasa batun yarjejeniyar.

A cikin jawabin sa a lokacin wannan zama, Firaministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn wanda shi ne shugaban kungiyar IGAD a wannan karon ya ce wannan muhimmin mataki ne na zuwa gaba da aka samu a takaddamar da kasar ke fama da shi cikin watanni 20. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China