in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jarin da Sin ke zubawa a nahiyar Afirka karkashin bankin CDB zai kai dala biliyan 5
2015-07-02 19:20:11 cri
Sabon shugaban asusun zuba jari domin ci gaban Sin da nahiyar Afirka ko CAD a takaice, Mr. Shi Jiyang, ya ce a wannan shekara da muke ciki, yawan jarin da Sin ke zubawa karkashin asusun sa, wanda bankin samar da ci gaban kasar Sin (CDB) ke gudanarwa, zai kai zunzurutun kudi har dalar Amurka miliyan dubu biyar.

Mr. Shi ya bayyana hakan ne ga wani taron manema labaru, bayan kammala taron yini biyu game da harkokin zuba jari a Afirka, wanda bankin duniya, da bankin samar da ci gaba na Sin, tare da wasu cibiyoyin kudi suka yi hadin gwiwar shiryawa a birnin Addis Ababan kasar Habasha.

An dai kafa asusun CAD ne a shekarar 2007, domin fadada hanyoyin bunkasa zuba jarin kasar Sin a nahiyar Afirka. Kuma ya zuwa yanzu, asusun ya shigar da kudade har dalar Amurka biliyan 2.3, a wasu ayyuka 80, wadanda suka hada da na samar da ababen more rayuwa, da harkar noma, da makamashi, da samar da lantarki, da masana'antu a kasashen Afirka sama da 30.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China