in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fara yin amfani da dakin gwaji na tafi-da-gidanka don binciken zazzabin cizon sauro a Afirka
2015-02-09 16:18:01 cri
Tawagar likitocin da kasar Sin ta tura a kasar Saliyo ta gano kwayoyin cutar zazzabin cizon sauro cikin jinin wasu mutane 3, a daren ranar Asabar da ta gabata, wanda ya kasance karon farko da kasar Sin ta yi amfani da dakin gwajinta na tafi-da-gidanka domin gudanar da aikin bincike kan cutar Malaria a nahiyar Afirka.

Likitocin kasar Sin sun fara wannan aiki ne bisa rokon ma'aikatar lafiya ta kasar Saliyo, wadda ta bukaci likitocin da su fara binciken kwayoyin cutar Malaria tare da na cutar Ebola a ranar Asabar 7 ga wata, sa'an nan za su mika duk sakamakon da suka samu ga hukumomin kasar a kai a kai.

A cewar Fang Tongyu, shugaban tawagar likitocin kasar Sin, a kan yi binciken jinin mutane kimanin 200 a ko wace rana a kasar ta Saliyo, sa'an nan a mako guda da ya wuce, yawan mutanen da aka gano dauke da cutar Ebola a ko wace rana bai wuce 20 ba, hakan na nuna cewa yanayin bazuwar cutar Ebola na raguwa a kasar, kuma sannu a hankali za a kawo karshenta.

Tun da likitocin kasar Sin masu kula da aikin binciken cututtuka da dakin gwaji na tafi-da-gidanka suka isa kasar Saliyo a watan Satumba da ya wuce, ya zuwa yanzu sun riga sun gudanar da bincike kan jinin mutane 4272, daga cikinsu 1416 suka kamu da cutar, kana binciken da likitocin kasar Sin suke yi a wannan kasa ya cimma nasara sosai, ba su taba yin kuskure ba. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China