Bisa labarin da wakilinmu ya samu daga ma'aikatar al'adun kasar Sin jiya Litinin 19 ga wata, an ce, za a shirya bukukuwan al'adun kasar Sin na shekarar 2015, da kuma bikin al'adun na "shekarar Sin" a Afirka ta Kudu, wadanda za a yi a nan kasar Sin da kuma kasashen Afirka fiye da 20, inda za a nuna wasannin fasaha, da taron kara wa juna sani, da makon nuna fina-finai, gami da cudanyar al'umma, cikin ayyuka kimanin 200.(Kande Gao)