in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun kama wani babban kwamandan Boko Haram
2015-08-03 19:07:02 cri
Rundunar sojojin Najeriya ta bayyana cewa, dakarunta sun yi nasarar dake wani babban kwamandan mayakan Boko Haram a jihar Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Wata sanarwar da rundunan sojojin kasar ta fitar ta bayyana cewa, an damke kwamandan kungiyar da ba a bayyana sunansa ba a wani samame da ta kaddamar a karshen makon da ya gabata a wata maboyar 'yan ta'addan da ke Aulari a yankin Bama da ke jihar ta Borno.

Kakakin runduna ta 7 ta sojojin Najeriya Kanar Tukur Gusau ya bayyana cewa, dakarun sun kuma yi nasarar tarwatsa sansanonin mayakan a sama da kauyuka 9 da ke yankin da ke fama da rikicin na Boko Haram.

Kungiyar Boko Haram dai ta halaka mutane sama da 13,000 kana da dama sun jikatta a hare-haren da ta kaddamar a cikin shekaru 6 da suka gabata.

Kungiyar ta kuma zafafa hare-haren da take kaddamarwa a arewa maso gabashin Najeriya, tun lokacin da aka rantsar da shugaba Muhammadu Buhari a watan Mayun wannan shekara, inda ya lashi takwabin kawar da kungiyar. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China