in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Batun yaki da Boko Haram zai kankame ziyarar shugaban Benin a Najeriya
2015-08-23 12:57:17 cri
Shugaban kasar Benin Boni Yayi zai kai wata ziyarar aiki a ranar Talata mai zuwa a Tarayyar Najeriya, inda zai tattauna tare da takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari kan matsalar tsaro a shiyoyin yammacin Afrika da kuma tsakiya, musammun ma kan yaki da kungiyar Boko Haram, a cewar wata majiyar diplomasiyya a birnin Cotonou a ranar Asabar.

Kasar Benin ta bayyana goyon bayanta ta hanyar aike da wata rundunar sojoji dake kunshe da mutane 800 a kusan takwarorinsu na Najeriya, Nijar, Kamaru da Chadi, a karkashin rundunar hadin gwiwa da za ta fara ayyukanta nan da 'yan kwanaki masu zuwa domin ganin an kawo karshen kungiyar Boko Haram baki daya.

Haka kuma wannan majiya ta nuna cewa, shugaba Boni Yayi zai yi shawarwari tare da gwamnan jihar Kebbi, Abubakar Atiku Bagudu, kan batun cigaban dangantakar kusanci tsakanin Benin da jihohin tarayyar Najeriya.

Dangantaka tsakanin Benin da Najeriya na dogaro kan wasu takardun doka goma, wadanda suka hada da dangantakar taimakon juna, zuwa yarjejenoyin dangantakar tattalin arziki, kimiyya da fasaha. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China