in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardar MDD zai kai ziyara a Najeriya
2015-08-22 13:38:17 cri
Magatakardar MDD Ban Ki-Moon zai kai ziyarar aiki na yini biyu a Najeriya ranar Lahadin nan, kamar yadda ma'aikatar harkokin wajen kasar ta tabbatar a ranar Jumma'an nan.

A lokacin ziyarar tashi, magatakardan zai gana da gwamnonin jihohin kasar 36 karkashin taken "samar da hanya ma sabuwar Najeriya: matsayi na gwamnatocin en'e-en'e", in ji bayanin da ke kunshe a sanarwar ma'aikatar harkokin wajen.

Babban jami'in majalissar har ila yau zai aiwatar da bikin saka fure domin juyayin shekaru hudu na harin bam din da aka kai a ofishin majalissar dake Abuja, sannan zai aiwatar da sauran ziyarce-ziyarcen aikin shi.

Bayan haka akwai wassu tattaunawa biyu a kan tattalin arziki da demokradiya a Najeriya wanda ake sa ran Mr Ban zai halarta. Muhimmin abin da zai yi lokacin ziyarar shi ne ganawa da Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari, wadanda suka gana a baya lokacin taron G7 na kwanan nan a kasar Jamus.

Shugaban na Najeriya da Babban magatakardan MDD za su kira taron manema labarai tare bayan ganawar tasu, in ji ma'aikatar harkokin wajen Nigeriya. (Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China